Jummaʼa 3 Yuli 2026 - 17:31
Jana'izar Shahidin Jagora Jari Ne Na Dabara Kuma Babban Makamashi Ga Gwagwarmaya"

Hauza/ Limamin Juma'ar birnin Qom ya bayyana cewa taron jana'izar Shahidin jagoran juyin juya hali jari ne na dabara ga nan gaba kuma babban madogarar makamashi ne ga harkar gwagwarmaya (Resistance). Ya ce wannan tafiya ce ta har abada da ke nuna wa makiyi cewa, ko da yake kuna son shafe shi, amma ta hanyar wannan tafiya ya mamaye dukkan kasashen musulmi kuma ya zama wani ra'ayi da ba ya taba kayuwa.

A cewar rahoton wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Ayatullah Sayyid Muhammad Sa'idi, a lokacin da yake gabatar da hudubar sallar Juma'a ta ranar 12 ga watan Tir na shekarar 1405 (03 ga Yulin 2026) a masallacin Quds na birnin Qom, ya bayyana cewa: "Taron jana'izar Shahidin jagoran juyin juya hali tare da iyalansa ba kawai sauya mazauni ba ne, a'a, taswirar hanyar ruhaniya ce."

Limamin na Qom ya ci gaba da cewa: "Fara ban kwana da gangar jikin a birnin Tehran yana da sako ga jami'ai da al'umma. Yin ban kwana a Tehran yana nufin cewa Shahidin jagoran juyin juya hali ya kasance tare da mutane duk da dimbin matsalolin da yake da su. Jana'izar a Tehran sabuwar rantsuwar mubaya'a ce ta mutane ga tafarkinsa da salonsa, da kuma ga Shugaba na Uku na Juyin Juya Hali, Hazrat Ayatullah Sayyid Mujtaba Khamenei, domin nuna wa makiyi cewa kisan gillar da aka yi wa mutum guda ba zai taba kaiwa ga kisan gillar manufofi ba."

Ya kara da cewa: "Jana'izar a Qom tana da alaka da haramin Ahlul Baiti (AS) da gidan Annabi, ziyarar Sayyida Ma'asumah (SA), da kuma alaka da Masallacin Jamkaran. Duk wadannan suna nufin komawa ga tushen ruhaniya na juyin juya hali da kuma inda aka assasa juyin juya halin Musulunci. Zuwan gangar jikinsa birnin Qom tamkar ziyarar mutanen da suke zuwa gurin sa a kowace shekara a ranar 19 ga watan Dey ne."

Limamin na Qom ya bayyana cewa: "Jana'izar wannan imami shahidi a Qom tana nuna muhimmancin fagen ilimi, yaki, da gwagwarmaya, kuma tana bayyana cewa ilimi ba tare da aiki da shahada ba nakasu ne. Kamar yadda Imam Hussain (AS) ya nuna mana wannan tafarki."

Ya kuma bayyana cewa: "Jana'izar a kasar Iraki ita ma ta mayar da al'amarin daga matakin kasa zuwa matakin al'ummar Musulmi gaba daya (Ummah); domin shi Shahidin jagoran juyin juya hali ya kasance jagoran al'umma ne. Wannan shi ne asalin alaka tsakanin makarantun koyarwa na Wilayah a Iran da kuma Haramomi masu tsarki na Wilayah da Imamanci a Iraki. Sakon wannan jana'izar shi ne cewa rundunonin gwagwarmaya ba yankin kasa ba ne kawai, a'a, tsari ne na imani wanda ya hadu tun daga Tehran har zuwa Qom, daga Najaf da Karbala har zuwa Mashhad, kuma ba ya taba rabuwa."

Limamin na Qom ya bayyana cewa: "Jana'izar a Mashhad komawa ce ga rungumar Imami na takwas (AS). Siffar zahiri ta jana'izar ita ce cewa isa Mashhad shi ne karshen tafiya, amma a zahiri shi ne farkon tafiya. Binnewa a haramin Imam Rida (AS) alama ce ta neman mafaka a guri mafi amintaccen mafaka ga al'umma."

Ya kara da cewa: Imam Reza (AS) ya ce:"Duk wanda ya ziyarci kabarina duk da nisan tafiya, zan zo masa a ranar kiyama a wurare guda uku har sai na cece shi daga firgicin wadannan wurare: lokacin da ake raba littattafan ayyuka ta dama da hagu, lokacin ketare Siradi, da kuma lokacin auna ayyuka (Mizan)."

Shugaban Haramin Sayyida Ma'asumah (SA) ya tuna cewa: "Babban abin farin ciki da ban mamaki a wannan taron shi ne yadda 'yan uwan iyalansa suka raka shi a wannan jana'izar, wanda hakan ya mayar da shi daga kisan siyasa zuwa fafatawar juriya irin ta Husaini, domin Imam Hussain (AS) shi ma bai kasance shi kadai ba a Karbala, har ma da jinjirinsa yana tare da shi."

Ya ci gaba da cewa: "Shahadar iyalan jagoran al'umma irin waccan sadaukarwa ce ta Ashura, kuma tana aika sako ga makiyi cewa lokacin da shugaba ya sanya dukkan iyalansa a tafarkin manufarsa, wannan yana nufin shugabanci a Musulunci ba shiri ba ne na neman mulki, a'a, soyayya ce ta isa ga gaskiya. Wannan mataki na sadaukarwa yana kore kowane irin shakku daga zukatan mabiya."

Wakilin jagoran juyin juya hali a Qom ya jaddada cewa: "Taron Jana'izar Imam Shahid jari ne na dabara ga nan gaba kuma babban madogaran makamashi ne ga harkar gwagwarmaya. Wannan tafiya ce ta har abada da ke nuna wa makiyi cewa, ko da yake kuna son shafe shi, amma ta hanyar wannan tafiya ya mamaye dukkan kasashen musulmi kuma ya zama wani ra'ayi da ba ya taba kayuwa."

Yayin da yake ishara da harin da jiragen ruwan Amurka suka kai kan jirgin saman fasinja na Iran a shekarar 1367 (1988) wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane sama da 290, sannan kai tsaye ya tunatar da gano makarkashiyar juyin mulkin Amurka a sansanin sojin sama na Nojeh, ya ce: "A yau, wane irin mataki ya kamata mu dauka da Amurka da irin wannan tarihi nata?"

Limamin na Qom ya ci gaba da cewa: "Mugun mutumin nan Trump, ta hanyar gabatar da yarjejeniya da alkawuran banza da kuma neman sayen lokaci, yana son ya bude mashigar Hormuz kafin zabukan da Amurka za ta yi a watan Nuwamba domin ya rage farashin mai da fetur, sannan bayan haka ya wargaza teburin tattaunawa ya kai wa Iran hari. Jamhuriyar Musulunci ta Iran, duba da rashin rikon amana ga alkawuran Amurka, ta mayar da batun yarjejeniya da tattaunawa a matsayin dama ta sake gina karfinta da kuma karfafa tsaron kasarta, kuma a halin yanzu tana cikin kololuwar shiri."

Ya ce: "Sakamakon tattaunawa a fili yake, Amurka ba za ta amince da yarjejeniya da tattaunawa ba, kuma Iran ba za ta taba janye jiki daga bukatunta na gaskiya ba. Wadanda aka ba su ikon tattaunawa da Amurka dole ne su kasance masu taka-tsantsan da wannan azzalumi mai karya alkawari; domin Allah madaukakin sarki yana cewa a cikin Alkur'ani: 'Kuma idan suka karya alƙawarinsu bayan yin alkawarinsu, kai tsaye suka soki addininku, to ku yaki shugabannin kafirci, domin lallai su ba su da wani alkawari, ko za su hanu.' (Suratul Tawbah: 12)."

Limamin na Qom ya kara da cewa: "Jami'anmu sun kuduri aniyar sanya bukatunsu na gaskiya a kan makiyansu, musamman Amurka da Sahyoniya, da kuma durmuza hancinsu a kasa."

Ya bayyana cewa: "A yau kasar mu, albarkacin wanda ya kafa juyin juya hali, Imam Shahid, da kuma Imam na yanzu, ta zama babban iko na hudu a duniya kamar yadda makiya da kansu suka amince; wani babban iko da ba ya gajiyawa wajen kwato hakkinsa da yaki da girman kai na duniya. Duniya ta sani cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta taba amincewa da kaskanci ba, domin ta koya daga Imam Hussain (AS) cewa: 'Haihata minaz zillah'."

Hudubar Farko: Yaki da Son Zuciya da Neman Natsuwar Ruhaniya

Ayatullah Sa'idi a hudubarsa ta farko ya bayyana cewa: "Kuka saboda Imam Hussain (AS) dole ne ya haifar da tsoron Allah (Takawa), wato bayan tarukan makoki mu kasance misali na fadin Imam Ali (AS) inda yake cewa: 'Ku kasance masu gaba da azzalumi kuma masu taimakon wanda aka zalunta'. Haka nan, bayan kammala tarukan, dole ne mu kasance masu azama a kan umarni da kyakkyawa da hani da mummuna, kamar yadda Imam Hussain (AS) ya bayyana cewa ya mike ne domin umarni da kyakkyawa da hani da mummuna. Domin majalisin Imam Hussain (AS) yana tsarkakewa kuma yana motsa mutum zuwa ga yin ayyukan farilla da nisantar abubuwan da aka haramta."

Ya ce: Allah madaukakin sarki yana cewa a aya ta 26 a cikin Suratul Fath: "A lokacin da wadanda suka kafirta suka sanya girman kai a cikin zukatansu, girman kai irin na jahiliyya, sai Allah ya saukar da natsuwarSa ga ManzonSa da kuma ga muminai, kuma Ya lizimta musu kalmar takawa, kuma sun kasance mafi cancanta da ita kuma ma'abotanta, kuma Allah Ya kasance Masani ne ga kowane abu."

Limamin na Qom, yayin da yake bayyana cewa girman kai na jahiliyya (Hamiyyah), natsuwa (Sakina), da tsoron Allah (Takawa) sune siffofi guda uku da aka ambata a cikin wannan aya, ya ce: "Kalmar Hamiyyah tare da sharadin jahiliyya tana nufin son zuciya da taurin kai da ba su da ma'ana."

Ya ci gaba da cewa: "Mushrikan Makka sun damu da cewa idan suka bar Annabi (SAWA) ya shiga Makka ya gudanar da ayyukan hajji, mene ne zai zama ra'ayin mutane game da mu? Domin kafin wannan lokaci Annabi (SAWA) ya yi hijira a asirce daga hannun mushrikai ya koma Madina. A nan ne girman kai na kabila da kishin jahiliyya ya zo wa mushrikai domin su hana musulmi shiga Makka. Wannan kishi da taurin kai ya bayyana kansa a lokatim tattaunawa da tsara yarjejeniyar sulhun Hudaibiyyah."

Limamin na Qom ya bayyana cewa: "Kasancewar wannan mummunar dabi'a mai rugujewa a cikin kowane mutum ko al'umma yana haifar da masifa, domin yana sanya labule mai kauri a kan hankali da tunanin mutum, kuma yana hana shi fahimta ta gaskiya da kuma yanke shawara mai kyau."

Shugaban Haramin Sayyida Ma'asumah (SA) ya ce: "Mika al'adu marasa kyau daga wata al'umma zuwa wata yana faruwa ne a karkashin inuwar wadannan taurin kai na jahiliyya. Dagewar da al'umma karkatattu suke yi a gaban Annabawa yana faruwa ne sakamakon wannan siffa. Misali, a lokacin da ake tambayarsu me yasa kuke bautawa gumakan da kuka kera da hannunku, sai suce: 'Shin kuna son ku hana mu abin da muka samu iyayenmu a kansa ne?' Wato suna fifita al'adun iyayensu a kan hankali da basirar su."

Ya bayyana cewa: Imam Sajjad (AS) ya ce game da son kai (Asabiyyah): "Son kai da mai shi yake yin laifi a kansa shi ne mutum ya ga miyagun mutanen mutanensa sun fi nagartattun mutanen wata al'umma kyau. Ba laifi ba ne mutum ya so mutanensa, amma son kai (na laifi) shi ne mutum ya taimaki mutanensa a kan zalunci."

Limamin na Qom ya kara da cewa: "Tushen yaki da barna sau da yawa shi ne wannan dabi'a. Muna ganin misalinta a cikin halayen Sahayoniya (Isra'ila). A gaban wannan mummunar dabi'a, Allah ya saukar da natsuwa da kwanciyar hangali a cikin zukatan muminai. Wannan natsuwa da kwanciyar hankali an haife su ne daga imani da dogaro ga kasancewar Allah da taimakonSa."

Wakilin jagoran juyin juya hali a Qom ya bayyana cewa: "Imani da dogaro ga Allah, yin biyayya ga hukuncin Allah da shugabancin Musulunci shi ne kadai maganin mummunar dabi'a ta son zuciya. Duk lokacin da mutum a lokacin kololuwar rikici ya sami damar kiyaye kwanciyar hankalinsa na ciki ta hanyar dogaro ga Allah, ikonsa na yanke shawara mai kyau yana karuwa. Yayin da abin da yake cikin zukatan kafirai na fushi da kiyayya ya kasance yana haifar musu da kura-kuran lissafi da shawarwari masu cutarwa."

Ya bayyana cewa: "Shaidan ya ce wa Annabi Musa (AS): "A lokacin fushi da bacin rai ka yi hattara da ni, domin raina yana cikin zuciyarka, idona kuma yana cikin idonka, kuma ina kewaya dukkan jikinka kamar jini domin in tumbuke tushenka ta hanyar gatari na fushi."

Limamin na Qom ya tunatar da cewa: "Kafiran Makka a lokacin sulhun Hudaibiyyah sun fahimci cewa dukkan kokarinsu na shafe Musulunci ya gaza, kuma sun kasance cikin fushi cewa juyin juya halin Musulunci na Annabi Muhammad (SAWA) yana ci gaba da yaduwa. Kafiran Kuraishawa sun ga kansu a matsayin wadanda suka yi rashi a gaban Annabi, shi ya sa suka rika yin abubuwa marasa ma'ana."

Yayin da yake bayyana mafi muhimmancin sakon wannan aya, ya ce: "A cikin labarin Hudaibiyyah, imani da dogaro ga shugabancin Annabi (SAWA) da daidaitattun shawarwarinsa sun kasance sanadin samar da natsuwa a cikin zukatan muminai. Wannan yana koya mana cewa a yau ma, yin biyayya ga Waliyyul Faƙih, Ayatullah Sayyid Mujtaba Khamenei, ita ce kadai hanya ta samun kwanciyar hankali da kuma hana girgiza a lokacin guguwar siyasa da ta al'umma."

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha